Wednesday, 1 March 2017

Bayani dangane da abinda yashafi habbatisauda, da kuma manta.

Muujizati Shifaa

Muujizati shifaa :littafin daya tattara bayanai akan yadda zaa iya neman waraka tahanyar amfani da
Habbatirashad
Tafarnuwa
Albasa
Zuma
 
Wanda wani bawan ALLAH balarabe mai suna Abul-fidaa MUHAMMAD azzat MUHAMMAD Aarifi yarubuta.
Allah yasaka masa da alkairi Ameen.

Bayani ko wata hikaya dangane da wani bawan ALLAH wanda Allah madaukakin sarki yajarabce shi da gudawa wanda taki tsayawa har kusan wata (6)wanda yake dayane daga cikin mazauna kasar masar.

Tsira da aminci su tabbata ga shugaban Annabawa da manzanni, shine shugabammu mai sammu mai kaunar mu, kuma abin kaunarmu Annabi MUHAMMAD saw. Tare da Iyalan gidan sa baki daya, da sahabban sa.
************************************

Dafarko abinda wannan bawan ALLAH yafara cewa.......

<<<<<<#Al-habbatisauda_dakuma_zuma>>>>>>

Yace hakika wadannan abubuwan kwara biyu #Habbatisauda da kuma zuma yace wallahi sunada matukar faida da kuma babbar falala da daraja agareni?????????? Badan komai yafadi hakaba sai don tsabar Faidar su daya gani sunyi masa, shi ne yasa shi yake ganin cewa kamar dama don shi kadai aka yo su!!!

Yace nakasan ce nakamu da gudawa mai tsananin gaske har tsawon wata shidda bata yanke ba, yace naje wajen likitocin daban daban suna rubuta man magungunan dake tsayar da gudawa naje nasiyo nasha, amma da zarar nagama sha kafin zuwa wani lokaci sai takara dawowa yadda take kamar bansha maganiba.........

Yace haka naci gaba da kasance wa acikin wannan halin, bayan haka wani likitan gona, kuma masani ta abangaran abinda yashafi jini, da fitsari, shi ma yadebi jini na, da kuma fitsari na domin ya gwada yaga cewa wacce irin cuta ce wanda take haifar man da wannan matsala
Bayan wannan likitan yagama bincike akai sai ya tabbatar da irin matsalar da take daymuna daga nanne nafara jin dadi cewa matsalata tazo karshe!!!

Sai dai akar she wani babban abinda yakara tada mun da hankali shine, bayan dana gama amfani da magungunan daya bani, kawai sai wannan gudawa takara dawowa kamar yadda take!

Nakoma wajan wannan likitan daganan yafada man cewa lallai babu makawa akwai abin lura dangane da uwar hanjin ka, da babban hanjin ka (large intestines) wata kila kodai akwai ciwo aciki ajikin sa, kokuma kuraje acikin ajikin su!!!

Ikon Allah daganan ne babban bakin ciki yasameni, da kuma babbar damuwa wanda tasanya na dimauce, amma duk da haka batasa na yanke tsammani daga rahamar ALLAH ba dangane da samun waraka daga wannan matsalar tawa!

Daganan nafara nazari dakuma tunani cewa kodai naje naga babban  
Likita Dr. Hassan Alhijari, likitan daya kware bangaran Cutuka wadanda baagane kansuba, dakuma bangaran matsalar Ciwon zuciya.

Amma shi wannan likitan yana yima marsa lafiyar sane magani da itatuwa, da kuma ganyayyaki, na muslunchi, da kuma asalin zuma, da hanyoyin neaman waraka wanda mutanan kasar China suke amfani da Ita.
Domin shi baya amfani da magungunan wadanda aka sarrafa su da ainufin chemicals, sai dai lokaci lokaci.

Danaje wajensa sai nadauki kwalbar zuma, yana kallona sai yace ga maganin ka nan a hannun ka kana rike dashi!!!

Kabar magani a gefen ka kana ta wahala kawai!!!

     Daga gobe na hore ka da kasha karamin kofin zuma dukkan bayan awa (3)haka zaka cigaba da yi har zuwa kwana daya.

Bayan haka sai kasamo #Huran_albabunaj katafasa sai katace kazuba cokali daya na zuma kasha kafin kaci abinci daawa daya...... Ikon daganan sai naji nafara samun yanayi mai dadi lafiya tafara samuwa kadan, amma dai wannan gudawa bata tsayaba baki daya.


Daganan sai wani abokina yabani wannan littafin mai suna ((Muujizati shifaa))

 
Daganan kawai sai gashi nasami abinda nabata acikin sa wajen neman sa, Yace sai nasamo man #Habbatisauda kawai kai tsaye nakama yin magani dashi,kamar yadda aka fada acikin wannan littafin, daganan cikin Ikon Allah gudawa tatafi baki daya bayan kwana uku dafara amfani da man habbatisauda,wanda yake na kwashe sama da wata biyar inafama  da Ita bata tsayaba.

Yace :Daganan nacigaba da cin kowanne kalar abinci, nasami lafiyar jikina fiye da shekarun da suka gabata.

Yace alal hakika bazan iya suffan ta irin yadda habbatisauda tazama magani mai ban mamaki wajan magance mun dukkan rashin lafiya ta ba.

Yace wannan abinda najarraba, don haka nabada ta sadaka ga dukkan wani mara Lafiya wanda yarasa magani daga Ciwon sa bayan duk yayi iya bakin kokarin to ga hanya sadaka. 

Yace Allah shine wanda yake me tabbatsr da shaida akan abinda nafada. 

Dafatan ALLAH yasaka masa da alkairi Allahumma Ameen. 

Rahamaniyya Islamic medicine Centre Funtua. 

Twitter @likitanci. 

Whatsapp 08152753609.

rahamaniyyaharbalmedicine.blogspot.com

Guzurin mamaci bayan mutuwar sa!!! (3)

Guzurin mamaci bayan mutuwar sa!!! Na (3)
************************************

Hadisi ya tabbata acikin Sahihi MUSLIM (RA) daga hadisin #Jarir_dan_Abdullah Yace :Manzon ALLAH saw. Yace:((lallai dukkan wanda ya tabbatar da wani aiki na alkairi kyakyawa acikin muslunci to bashakka yanada lada, da lada ga dukkan wanda Yayi koyi dashi na wannan kyakyawan aikin dakayi, amma batare da antauye ladar wadanda sukayi koyi da shiba, wannan kyakyawan abun alkairin daka aikata ba, aa ladar da zaa baka kaida kafara gaba tar da wannan abun alkairin,ko aikin daban, suma wanda sukayi aiki dashi ladar su daban, domin baa cikin ladar su zaa diba abaka ba na koyin dasukeyi dakai!!!

Haka kuma dukkan wanda yafara asassa wani mummunan aikin nasharri, ko sabon Allah madaukakin sarki, ko wani fasadi to zaa bashi mummunan sakamakon wannan aikin nasa daya kirkira.

Bayan haka kuma zaarika dora masa wani zunubin ga dukkan wanda yayi koyi ko yaaikata irin wannan aikin sharri daka gina ka kirkira, duk wanda yayi koyi dakai abayanka to sai anrubuta maka zunubi kaima akai, tare da cewa zunubin wanda yai koyi dakai daban, kuma zunubin da zaa rubuta maka daban na koyi da sukayi dakai, batare da antauye nasu zunuban ba.!!!!

Ubangiji Allah yamana tsari yakare mu Allahumma Ameen.

Alal hakika ire iren wadannan maanoni na wannan hadisin Antarosu dayawa daga manzon ALLAH saw. Ta fuskoki dadama, Kuma wadanda suke kyawawa,masu inganci.

Sahihi Muslim (3/1255)Babi wanda yake bayani abinda dan adam yake samu na lada bayan mutuwar sa.

Hakika wannan dalili yake nuna mana cewa kan magana na manzon ALLAH saw. Bazaa taba kashe wata rai bisa zalunci ba, face sai Allah madaukakin sarki yadora wani zunubin akan dan adam nafarko wanda yafara sunnanta kisan kai, domin shine wanda yafara gabatar
da wannan mummunan aikin!!!

To idan wannan bayani yakasance tafuskar yin azaba, da kuma ukuba, ko sakamako, to alal hakika abinda yake mafifici akai shine wajan samun falala, da kuma samun lada, ko sakamakon,na irin haka.

Maana idan kafara akata wani aikin sharri to dukkan wanda yayi koyi dakai abayanka to kana da zunubi...... To tunda Hakane wannan yanuna mana cewa kenan ina ga wanda yafara gabatar da wani aiki na alkairi kenan shine yafi cancanta da kuma dacewa asami sakamako.

Wallahu taala aalam.

Ya Allah kabamu Ikon kirkira abin alkairi, ko aiki na alkairi wanda yan bayan mu zasu amfana dashi, domin muma mu amfana dashi koda bayan mutuwar mu Allahumma Ameen.

Treat your sick by giving sadaqah!!!


Treat you sick by giving sadaqah!!!

1 - From Abu Umamah -Radi Allaahu anhu-who said: the Messenger of Allaah -sallAllaahu alayhi wa sallam- said:‘Treat your sick by giving Sadaqah (charity).’

[Collected in Saheeh al-Jamia’ No. 3358 & declared Hasan by Albaani]

2 - From Ubadah bin Saamitt who said I heard the Messenger of Allaah -sallAllaahu alayhi wa sallam- saying: ‘There is no person who is afflicted with a wound on his body, and he gives charity due to that, then Allaah Expiates from him the like of what he gave in charity.

[Collected by Ahmad & Albaani declared it to have an authentic Isnaad in Saheehah No. 2273]

3 – A man asked Abdullaah bin al-Mubarak -Rahimullaah- about ulcers that had sprung out on his knee for about seven years, and he tried to treat it with various treatments, he had asked doctors but to no avail. So Ibn Mubarak said: ‘Go and dig a well in a place where people need water, indeed I hope that there springs up water there, and by that you stop bleeding.’  The man did that and Allaah Ta’ala Cured him.’

[Taken from: ‘Seerah ‘Alaam’ 8/407]

Al-Bayhaqi quoted a story of our Shaykh al-Haakim Abu Abdullaah -Rahimullaah- who was afflicted with ulcers on his face, and he had tried a number of treatments but they did not go away, and it remained like that for nearly a year.

He then asked the teacher, Imam Abu Uthmaan as-Sabooni to make Dua’ for him in one of his gatherings on Friday, so he made Dua’ and many of the people with him said Ameen.  When it came to the next Juma’ a woman came to the gathering and left a brief message saying that she had gone back home and exerted herself in making Dua’ for al-Haakim Abu Abdullaah that night, and that she had seen the Messenger of Allaah -sallAllaahu alayhi wa sallam- in her sleep, and it was as if he was saying to her: tell Abu Abdullaah to distribute water amongst the Muslims.

I came with that message to al-Haakim, and he ordered that a watering place be built at the door of his home, when they had finished building it, he ordered for water to be poured into it and ice placed into that water, and then the people began drinking from that water.  Not a week had passed by, except that it was obvious that his health had been restored, and the ulcers had ceased. His face had become better than it was before, and he lived like that for a number of years.’

[Collected in ‘Saheeh Targheeb wa Tarheeb’ No. 964 Albaani declared it to be Saheeh Maqtu, 1/p.568]

4 - Abu Tahir as-Silafee said in ‘Mua’jam as-Safr’: I heard Abu Hasan Ali bin Abu Bakr Ahmad bin Ali the scribe of al-Minzi in Damascus saying: I heard Abu Bakr al-Khabazi (d. 449A.H.) in Nisaboor saying: I became sick with a very dangerous illness, and a righteous neighbor of mine saw me and said: ‘Utilize the saying of the Messenger of Allaah -sallAllaahu alayhi wa sallam-: ‘Treat your sick by giving Sadaqah (charity).’

It was summer time, and I bought many watermelons, and a group of poor people and children got together and ate them, then they raised their hands to Allaah –Azza wa Jal- and they made Dua’ for me to be cured.  I swear by Allaah I had not reach the morning except that I regained complete health from Allaah -Tabaraka wa Ta’ala.

[Seerah ‘Alaam 18/44, Tareekh al-Islaam]

5 - al-Barzali (d. 841A.H.) said in his Fatwa (5/612): Ibn Rushd was asked about the saying of the Messenger of Allaah -sallAllaahu alayhi wa sallam-: ‘Treat your sick by giving Sadaqah (charity).’ Is it authentic or not? And what does it mean? And if a person becomes sick and treats his illness with all types of medicines and they did not benefit him, then what is the way of giving Sadaqah as a medicine?

He answered:

‘I do not remember this text (narration) in any of the authentic collections of narrations, however, if it is authentic, then the meaning is an encouragement to visit the sick, because it is from the obligatory rights from the Sunnah that it is upon a Muslim that he visit a Muslim if he becomes sick.

As for the saying ‘The Muslim is a brother of a Muslim, he encourages him to say the testification at the time of death, and he visits him when he is sick, and advises him when he is absent or if he has to testify.’ As for visiting him then this is a good deed, and every good deed is Sadaqah, since it has a connection with the sick person and visiting him brings happiness to him, and just like making Dua’. There is no doubt that there is hope that the Dua’ will be answered and he will be cured.  Therefore, it does benefit him as a type of medicine, due to the saying of the Messenger -sallAllaahu alayhi wa sallam-: ‘He who sent down the illness also sent down the treatment.’

Al-Barzali said: some of our shaykhs from al-Qarawan understood this to have an evident meaning, namely that if a person gives Sadaqah on behalf of the sick, and that he requests the person whom he gave Sadaqah to, to make Dua’ for the sick then it is hoped that he will be cured, due to the saying of the Messenger -sallAllaahu alayhi wa sallam-: ‘The supplication of one of you for his brother in his absence is answered.’

6 – ad-Dooree narrated in ‘Tareekh’ and al-Bayhaqi in ‘Shu’ab al-Eemaan’ from Ibraheem an-Nakhai who said: ‘that the Companions used to regard giving Sadaqah as a means of repelling oppression.’

7 – From Hudayfah -Radi Allaahu anhu- that the Prophet -sallAllaahu alayhi wa sallam- said:

‘A fitnah (trail) which a man faces with regard to his family, his wealth, his own self, his son and his neighbor is expiated by fasting, prayer, charity, enjoining good and forbidding evil.’

[Collected by Bukhari & Muslim]

8 – Shamsuddeen Muhammad bin Abee Bakr Ibn Qayyim aj-Jawzeeyah (d.751 A.H.) -Rahimullaah- said:

‘Indeed Sadaqah has an amazing effect in repelling different types of trials and tribulations, even if the charity was given by an evil person, or an oppressive person, in fact even if it was given by a non-Muslim! Indeed Allaah Ta’ala repels different types of trials and tribulations due to giving Sadaqah.  This is a matter which is well-known to the scholars and the general folk, and all of the people on the earth can associate with this fact because they have experienced it.’

[Taken from: ‘al-Wabil as-Sayyib’ p.63]

9 – Shamsuddeen Muhammad bin Abee Bakr Ibn Qayyim aj-Jawzeeyah (d.751 A.H.) -Rahimullaah- said:

‘There are types of medicines which can treat illnesses which the minds of the senior doctors cannot comprehend, and that which their sciences, experiences and measurements cannot reach. These are the medicines of the heart and soul, and the strength of the heart, its dependence upon Allaah and trust upon Him and seeking refuge in Him. Prostrating and feeling in dire need of Allaah and humbling oneself for Allaah. Likewise giving Sadaqah (charity), making Dua’, repentance and seeking forgiveness, being good to the creation, aiding the distressed and liberating from grief and unhappiness.

Indeed these types of medication have been used by various nations, who are upon different religions and communities, and they found that they had an effect in the treatment of illnesses, which even the sciences of the most knowledgeable doctors could not reach, and they have no experience nor measurement of it. We have indeed experienced these matters a great deal and as others have, and we have seen what ordinary medicine can and cannot do.’

[Taken from: ‘Zad al-Ma’ad’ 4/11-12]

Guzurin mamaci bayan mutuwar sa kashi na (4)

Manya manyan dalilai da suka zo daga cikin alqurani, da sunna  da ijmain maluma, da kuma kawaid na Sharia wadanda suke nuni akan wadanda suke mutu suna samun lada tahanyar ayyukan wadanda suke raye......

Kamar Allah madaukakin sarki yafada acikin suratul hashar aya(10)

Allah madaukakin sarki yace "wadannan wadanda suke biyo bayansu suna cewa ya ubangijin mu kayi mana gafara, tare da yan uwan mu wadanda suka rigaye mu wajan yin imani...... "Allah yana yabon mu tahanyar yima bayin Allah wadan da suka riga mu yin imani tun farko ,sune sahabban manzon ALLAH saw. Domin haka manzon ALLAH saw. Yafada fiyayyun alumma sune wadanda sukayi zamani dani..... To wannan dalili yanuna cewa dalilin rigayar mu imani shi yasa ubangiji yasanya suna amfana da istigfarin mu, da kuma neman gafara da muke yi muna hadawa dasu aciki.
والذين جاءوامن بعدهم ربنااغفرلنا ولاخواننا الذين سبقونا بالإيمان....... الا ية.
Don haka indai kayi istigfari to suma suna da nasu rabon aciki na abinda suka kafa na alkairi, kuma nasu ba zai sa atauye nakaba.

Kamar yadda maluma sun tattaru basuyi sabani ba wajan yima mamaci aduah tahanyar roka masa gafara alokacin daake yima sa SALLAH.

Hadisi ya tabbata daga sunan na Abu Dawud (rahimahullah) Daga hadisin na Abu huraira (RA) yace :manzon ALLAH saw. Yace ((Idan zaku sallaci mamaci to kukebanta wajan yi masa addua,tahanyar roka masa gafara.

Bayan haka Anrawaito wani hadisi acikin Sahihi Muslim daga hadisin Aufi dan MALIK (ra) yace:wata rana manzon ALLAH saw. Yanayin sallatar wata gawa, sai muka kiyaye wani abu daga cikin adduoin dayarika yi, yana cewa "((Ya ubangiji  kayi gafara agare shi, kajikan sa, kayi masa rangwame, ka kuma saukaka masa, ka girmama masaukin sa, ka yalwata masa shi, kawanke shi daga dukkan zunubai, da ruwa, da kankara, da sanyi ka kuma tsarkake shi daga kurakuransa daya aikata sukoma fari fat,kamar yadda muke wanke farin tufafi daga datti, kuma ka canza masa gida wanna yafi gidan sa na duniya, ka canza masa Iyalan sa fiye da iyalinsa dayabari a duniya, ka canza masa mata fiye da matar sa ta duniya, ya Ubangiji muna rokonka kashigar dashi aljanna, kayi masa kariya daga azabar kabari.

Dafatan ALLAH ubangiji yayafe mana dukkan kurakuranmu zahiri ,da badini, Ya Allah ka kyatata karshen mu kasa mucika da imani. Ka gafar ta ma dukkan mamatan mu musulmi maza da mata Allahumma Ameen.