Alal hakika wajibine kamewa acikin Ramadan tun daga bullowar alfijir,har zuwa lokacin da rana zata fadi.
Kamewa daga ci,da sha,da kuma yin jimai awannan lokacin,dadai sauransu.
To menene hukuncin wanda yaci,ko yasha acikin ramadan da rana bisa ga mantuwa amma daga baya ya tuna.Bisa ga zance mafi inganci daga bakin maluma shine,idan mutum yaci,ko yasha acikin watan ramadan da rana da gangan to wannan sai yayi kafara azumi (60)Ajeri sannan kuma yarama dayan.
Amma idan bisa kuskure ne to akace babu laifi,maana bazaiyi koda ramuwa na wannan azumin,kuma bazaiyi kaffara ba.Saboda akwai hadisin daaka samu daga Abu huraira (RA)yace:Manzon Allah saw.yace :"Dukkan wanda yamanta cewa yana azumi sai yaci,ko yasha to yacika sauran azumin,maana yaci gaba yakai wannan azumin,domin Allah ne yaciyar dashi,kuma yashayar dashi"
Bayan haka jawo amai da gangan,shima yana karya azumi,amma wanda amai yarinjaye shi batare da son ransaba to akace wannan babu laifi akansa bazai ramuwar wannan azumin ba,kuma bazai yi kaffara ba.
Ansamo wani Hadisi daga Abu hurara(RA)yace :Hakika manzon Allah saw.yace "Dukkan wanda amai ya gangaro masa hakanan to babu ramuwa akansa,amma dukkan wanda ya kakalo shi da gangan to yarama wannan azumin.
Bayan haka Jinin haila,da kuama jinin haihuwa koda koda gab da zuwa karshen yinine maana saura kadan rana tafadi sai yazoma mai yin azumi,bisa zancen maluma mafi inganci to wannan azumin babu shi,sai dai ayi ramuwarsa.
Yaku yan uwa hakika dukkan wanda Allah swt.ya hore masa yalwa to yakamata yarika taimakon wadanda suke da rauni basuda abin zasu anjima balle na gobe,domin wannan lokaci lokaci mai tsada,domin ciyarwar acikin watan ramadan,ko kuma bayar da sadaka yafi lada bisa ga kowanne lokaci,kuma yin hakan yana daga cikin abinda Allah swt.ya umar ce mu da yinsa,domin haka yake fada ma dan karuun cewa "Ka kyatata ma alumma kamar yadda Allah ya kyatata maka tahanyar baka wannan wadatar,kada kazama mai yin fasadi abayan kasa,domin Allah bayason mai aikata fasadi wanda yake mabar naci"(Suratul kasas).
Wallahu taala aalam.
Ya Allah kayafe mana dukkan zunuban mu wadanda muka aikata su muna sane,da kuma wadanda muka aikata batare da munsan cewa mun aikata suba,ya Allah kasa muna daga cikin bayinka wadanda zaka yantar dasu daga shiga cikin azabar ka aranar alkiyama,ya Allah kabiya mana dukkan bukatunmu na alakairi,marasa lafiya ya Allah kabasu lafiya muda muke da ita ya Allah kakara mana ita,shuwagabbanin mu ya Allah kataimakesu kabasu ikon yin adalci agare mu,ya Allah kabama shugaban kasar mu lafiya,domin albarkacin sunayan yahayyu ya kayyumu ameen.
Dukkan abinda kukaga mun kawo anan to yananan acikin shafinmu mai suna
FATAWOWIN MAGABATA
Idan kuma kuna bukatar bincikowa kai tsaye to zaku iya rubutawa akan Google kai tsaye,kokuma ta wannan address dake kasa.
musluncitafarkintsira.blogspot.nl/?m=1