Zance mafi inganci inji maluma shine,duk wanda yazama yagajiya saboda tsufa baya iya yin azumi Ramadan,ko makamancin hakan to zai ci abinci,amma ana bukatar kuma kowacce rana sai yaciyar da miskini,saboda fadar Allah swt.((Cewa ga wadannan wadanda basa iya yin azumi,maana yin sa hakan zai sa susami wahala kwarai to zasu rika bada fidya kullum shine ciyar da miskini.))Bakara aya(184).
Ansamo wani hadisi daga Adain cewa yace yaji daga Dan Abbasu (RA)Yaji ana karanta wannan ayah((وعلي الذين يطيقونه فدية طعام مسكين))Sai dan Abbas (ra)yace:Wannan ayah baa shafe hukuncin taba,abinda take nufi maana shine tana nufin tsoho tukub,da kuma mace tsohuwa tukub,idan basa iya yin azumi,to abinda zasuyi shine kowacce rana sai suciyar da miskini.
Sahihul irawaa(912) Kuma wannan hadisi danganensa ingantacce ne daga ibni Jareer.(135/2)
Hakika wannan lokacine nasamun lada,don haka dukkan ibadar da kayi zaa ninka ma ita ne,don haka wanda Allah swt.ya hore masa dama da hali,to yatai maki bayin Allah gwargwadon iya warsa.
Domin awani Hadisi manxon Allah saw.yana cewa duk wanda yaya ye ma wani muimini wani bakin ciki daga cikin bakin cikin duniya,to Allah zai yaya ye masa bakin cikin duniya da lahira.
Domin ayyukan shiga aljannah basuda iyaka,bakasan cewa wanne aikine zakayi wanda zai kaika zuwa ga aljannah ba,domin dukkan ayyukan samun lada babu abinda yakai ciyarwa lada,ko shayarwa.
Dafatan Allah yabamu ikon yi ameen.
Wallahu taala aalam.
No comments:
Post a Comment