Tuesday, 6 June 2017

SUWANE NE AZUMI YA WAJWBA AKANSU?

Wadanda azumi yazama wajibi akansu suyi shi sune kama haka:((Bisa tattaruwar maluma akan wannan cewa azumi ya wajaba ne akan mutum wanda musulmi,kuma mai hankali,kuma baligi,wanda yake lafiyayye,wanda yake kuma azaune agari))

Dan haka azumi bai zama wajibiba ga wanda yake da tabin hankali.

Azumi bai zama wajibi ba ga wanda bai balaga.

Bayan haka azumi yawajaba akan mata,amma banda macen da takeyin jinin haila,ko na haihuwa,lallai dole har sai yazama mace tana da tsarki,daga jinin haila ko na haihuwa.

Amma abinda yake tabbatar da cewa azumi ba wajibi bane ga wanda yake da tabin kwakwalwa, kuma baligi,bisa fadar maaiki saw.((Ana dauke alkalami abin rubutu akan mutane kwara (3)
(1)Ana dauke abin rubutu akan wanda yake mai tabin hankali.

(2)Ana dauke alkalami abin rubutu akan wanda yake yin barci,har sai lokacin daya falka.

(3)Ana dauke abin rubutu akan yaro karami har sai lokacin da balaga yafara mafalki.

Amma akace anso ga wanda yake majibincin wannan yaron ko mahaifansa da suyi masa umarni dayin azumi gwargwadon yadda zai iya domin ya koya,hakan kuma yin koyine da Sahabatu rasulallah.Domin sahabban manzom Allah swa.suna ummartar yaransu dayin azumi.

Ansamo wani hadisi daga Rabii dan Muawiz tace:Cewa manzon Allah saw.Akwai wata rana daakayi gari ranar ashura ya aika zuwa yan kunan alansar cewa((Duk wanda yawayi gari yana cin abinci to yacika sauran abinda yaragu na wannan ranar,wanda kuma yawayi gari yana azumi to yacigaba da azuminsa))

Bayan haka tace kuma Mun kasance munayin azumi,kuma yaranmu ma sunayi,muna sasu sunayin wasa amma da zarar muka ga yaro zaiyi kuka to sai muce yaci abinci sai muba shi abinci.

Bayan abinda yasa akace azumi yawajaba akan wanda yake lafiyayye kuma baligi,wanda zaune agari ba matafiyi ba shine,wannan ya kafune bisa fadar Allah swt.((Cewa wanda yakasance mara lafiya daga cikinku,ko wanda akan hanyar sa ta tafiya to zai iya ajiye azuminsa,amma zai gididdige kwanakin dayayi domin yin ramuwa agaba.

Amma idan mara lafiya yaga zai iya yin azumi,koko mata fiyi yaga zai iyayin azumi to wannan babu laifi hakan yayi,domin damar daaka basu na suci abinci wannan rangwamene akayi masu,domin saukaka masu,amma idan sunga suna iyawa to hakika sundauki aiki mai girma.

Wallahu taala aalam.

Ya Allah kabiya mana dukkan bukatun mu na alkairi,kayafe mana zunuban mu zahiri,da badini,manya da kanana kara bautar damu da samun jinkan ka,da rahamarka,awannan wata mai alabarka ameen.

No comments:

Post a Comment