Wednesday, 7 June 2017

MENENE HUKUNCIN WANDA YACI ABINCI,KO YA SHA ABIN SHA DARANA ACIKIN RAMADAN BISA GA MANTUWA?

Alal hakika wajibine kamewa acikin Ramadan tun daga bullowar alfijir,har zuwa lokacin da rana zata fadi.

Kamewa daga ci,da sha,da kuma yin jimai awannan lokacin,dadai sauransu.

To menene hukuncin wanda yaci,ko yasha acikin ramadan da rana bisa ga mantuwa amma daga baya ya tuna.Bisa ga zance mafi inganci daga bakin maluma shine,idan mutum yaci,ko yasha acikin watan ramadan da rana da gangan to wannan sai yayi kafara azumi (60)Ajeri sannan kuma yarama dayan.

Amma idan bisa kuskure ne to akace babu laifi,maana bazaiyi koda ramuwa na wannan azumin,kuma bazaiyi kaffara ba.Saboda akwai hadisin daaka samu daga Abu huraira (RA)yace:Manzon Allah saw.yace :"Dukkan wanda yamanta cewa yana azumi sai yaci,ko yasha to yacika sauran azumin,maana yaci gaba yakai wannan azumin,domin Allah ne yaciyar dashi,kuma yashayar dashi"

Bayan haka jawo amai da gangan,shima yana karya azumi,amma wanda amai yarinjaye shi batare da son ransaba to akace wannan babu laifi akansa bazai ramuwar wannan azumin ba,kuma bazai yi kaffara ba.

Ansamo wani Hadisi daga Abu hurara(RA)yace :Hakika manzon Allah saw.yace "Dukkan wanda amai ya gangaro masa hakanan to babu ramuwa akansa,amma dukkan wanda ya kakalo shi da gangan to yarama wannan azumin.

Bayan haka Jinin haila,da kuama jinin haihuwa koda koda gab da zuwa karshen yinine maana saura kadan rana tafadi sai yazoma mai yin azumi,bisa zancen maluma mafi inganci to wannan azumin babu shi,sai dai ayi ramuwarsa.

Yaku yan uwa hakika dukkan wanda Allah swt.ya hore masa yalwa to yakamata yarika taimakon wadanda suke da rauni basuda abin zasu anjima balle na gobe,domin wannan lokaci lokaci mai tsada,domin ciyarwar acikin watan ramadan,ko kuma bayar da sadaka yafi lada bisa ga kowanne lokaci,kuma yin hakan yana daga cikin abinda Allah swt.ya umar ce mu da yinsa,domin haka yake fada ma dan karuun cewa "Ka kyatata ma alumma kamar yadda Allah ya kyatata maka tahanyar baka wannan wadatar,kada kazama mai yin fasadi abayan kasa,domin Allah bayason mai aikata fasadi wanda yake mabar naci"(Suratul kasas).

Wallahu taala aalam.

Ya Allah kayafe mana dukkan zunuban mu wadanda muka aikata su muna sane,da kuma wadanda muka aikata batare da munsan cewa mun aikata suba,ya Allah kasa muna daga cikin bayinka wadanda zaka yantar dasu daga shiga cikin azabar ka aranar alkiyama,ya Allah kabiya mana dukkan bukatunmu na alakairi,marasa lafiya ya Allah kabasu lafiya muda muke da ita ya Allah kakara mana ita,shuwagabbanin mu ya Allah kataimakesu kabasu ikon yin adalci agare mu,ya Allah kabama shugaban kasar mu lafiya,domin albarkacin sunayan yahayyu ya kayyumu ameen.

Dukkan abinda kukaga mun kawo anan to yananan acikin shafinmu mai suna
FATAWOWIN MAGABATA
Idan kuma kuna bukatar bincikowa kai tsaye to zaku iya rubutawa akan Google kai tsaye,kokuma ta wannan address dake kasa.
musluncitafarkintsira.blogspot.nl/?m=1


Tuesday, 6 June 2017

Fatawowin magabata

musluncitafarkintsira.blogspot.nl/?m=1

MACE MAI CIKI,DA KUMA WANDA TAKE SHAYARWA.

Mace mai ciki,da kuma wanda take shayarwa maluma sukace idan bazasu iyayin azumi ba,kokuma suka ji tsoro ga yaronsu to suci abinci,amma zasu bayar da  fansar wannan azumin,kuma babu ramuwa akansu.

Ansamo wani hadisi daga dan Abbas (RA)yace:((Anyi rangwame ga wanda yake tsoho,da kuma mace  tsohuwa awajan wannan,amma abinda yake akansu shine suci abinci kuma suciyar akowacce rana zasu ciyar miskini.Babu ramuwa akansu.wanda yake ada koda tsoho ko tsohuwa zasu iyayin azumi idan sunso suyi azumi,idan sunso suci abinci,sai suciyar da miskini akowacce rana sai aka shafe wannan da fadin Allah swt.cewa (Duk wanda yazama watan Ranadan yakama yanada cikakkiyar lafiya,da hankali,kumA baligi yazama wajibi yayi azumi))

Amma sai akayi rangwame ga mutumin dayake tsoho,ko mace tsohuwa idan basa iya yin azumi,da kuma mace mai ciki,da kuma wanda take shayarwa idan sunji tsoron cutarwa ga yayayan su to akace suci abinci,amma kowacce sai suciyar da miskini.

Bayan haka da kuma wani Karin bayanin daga dan Abbasu (RA)Yace ((Idan mace mai ciki taji tsoro akanta kada tasha wahala mai tsanani,da kuma mace mai shayarwa taji tsoro ga yaronta kada kada yasha wahala acikin watan Ramadan tahanyar rasa nonon da zai sha sai yace:to ya halatta suci abinci,kuma suciya da miskinai akowacce rana,kuma bazasu rama wannan azumin ba.

Ansamo wani hadisi daga Nafiu(RA)yace:((Wato yakasance wata diya daga cikin yayan dan Ummaru (RA)tana karkashin wani mutum bakurai she,kuma yazama tanada ciki acikin watan Ramadan,sai kishi yasame ta acikin wannan wata,kishi matsananci,sai dan Ummar ya ummar ceta dacewa taci abinci,kuma taciyar da miskini akowacce rana))

Wallahu aalam.
Ya Allah kagafarta mana zunubanmu gaba daya,kayi mana rahma,kabiya mana bukatunmu na alkairi ameen.

Yana daga cikin nauikana shirka na bokaye,dabkuma Arrafa,malamai yan duba!!!

Boka,da kuma malaman duba maganar gaskiya dukkansu sun kafurce ma Allah swt.saboda sunyin daawar sanin gaibi,abinda yake aboye ko zai faru jibi,nanda sati,shekara,ko shekaru,domin hakika sanin gaibi sai Allah.

Duk da cewa wasu maluma sukan kasa sanin gaibi kala daban,kamar alal misali Allah yakan sanar da annabawa wasu alamura ta hanyar wahyi daake yi masu.da dai sauransu.

Amma mafi yawa daga cikin gaibin da yan bori,da bokaye,da malaman duba suke daawar sanin sa badole bane yazama gaskiya,da yawa sunayin dubaru domin amsar kudin jamaa ne kawai wadanda suka rafkana,ta hanyar zana alkaluma,ko bugun ramli,kokuma duba hannun mutum,ko azuba ruwa a koko ko kwalba da sunan ganin matsalar mutum,koko madubi,da dai sauransu.

Domin bugun kasa duk da cewa irin harrufan alqurani ne ake bugawa suzama harrufa,to wannan ba dalili bane nayin haka,saboda ba shine manufar sanar da wannan ilimin ba,domin Allah swt.yace mun sanya ilimin hisabi ne,ba don ayi dubaba sai don kusan yawan kirgan shekaru,da kwanuka,da watanni.

Amma yanzu sai kaga anmai da abun sanaa,yanzu idan mutum yaje wajen neman magani,ko wata bukata in har wannan bokan,ko dan duban,ko dan bori bai iya wadannan dubarun ba,to bazai sami ko mai ba.......saboda tsabar imani da wasu daga cikin alumma dasukayi da hakan.

Kuma inda babbar illar take shine zaka gani sukan fahimci cewa menene kake so,to koda sunga cewa wannan abun ba zai yiwuba to bazaa taba fada maka hakaba,domin idan anfada maka gaskiya to bazaka bada kudi da yawaba,wannan dalili sai yasa afada maka karya domin kabada.

Kokuma koda anga cewa wannan bukata taka babu wata matsala zata yiwu sai ace kai ai dole sai anyi aiki akai,nanma afada maka karya kawai don a amshi kudinka,to wannan kuma ya shiga cikin saba ma Allah,domin yin karya haramunne a muslunci.Kaga daganan ata dalilin neman duniya mutum yazama makarya ci karfi da yaci.

Akwai wani babban mutum awannan kasar tamu da zan fadesa kowa zai san shi,domin yasami matsayi kala daban,daban wajen aiki,awani lokaci sai ya fito takara kuma yasa aka tara masa malamai irin wadannan masu yin duba din!!!

Kowa da ya buga kasa sai ai zaayi nasara babu makawa zai ci wannan zaben.
Sai wani malami shi kadaine yace aa gaskiyar magana babu nasara akan wannan tafiya,domin bazai ci wannan takaraba,yace kai karya kakeyi dukkan wadannan maluma kowa yace zaayi nasara sai kai kadaine zakace ba zaayi nasaraba,wannan ba gaskiya bane.

Saura aka basu buhunan shinkafa,da kudade masu yawa aka sallame su suka tafi.

Shi kuma da yace bazaayi nasara hakanan yata shi yatafi.
Anan nan anata yin kamfe akazo wajen yin zaben yan labai yafadi baiciba!!!Nan take yagane cewa sauran wadannan maluman karya suka fada masa kawai domin yabasu kudi.
Wannan dayan shi kadai ne yafadi gaskiya.

Domin manzon Allah saw.yace dukkan wanda yaje ma mace wanda take jinin haila maana yasadu da mace mai yin jinin haila,da kuma wanda yasadu da mace ta duburarta,da kuma wanda yaje wajen boka to yakafurta da abinda ka saukar agare shi.Allah yakare mu ameen.

Domin boka ko dan bori,ko malumin duba idan yafadi gaskiya sau daya to sai yayi karya sau( 99)Amma mutanen da suka rafkana zuciyar su ta dusa she bazasu gane hakanba.

Domin mutane suna zuwa wajen su domin sanin abinda zai faru agaba,da abin farin ciki,da kuma abun bakin ciki,imma tahanyar aure ko kasuwa,da bincike akan abinda yabata da dai sauransu.

Sannan kuma mutane sukan gaskta abinda aljannu suka fada abakin bokaye ko yan bori.Bil hasalima yanzu idan kana bayar da magani awajen wasu indai bawai kana da wasu shaidanun aljnnu dake ma wahyiba to basu dauka cewa kasan wani abu.Allah yakyata ameen.

Ban mantawa akwai sanda inayima wata baiwar Allah Ruqqa sai wannan  aljanin yace ai shi yana kareta ne ,badon haka da abun yayi tsanani sosai!!!Sai nace masa kai wayake kareka yace Allah,nace to itama Allah ne yake kareta.......kuma nanu na masa hakan amma yakasa ganewa.

Daga nan nace masa tunda kaki yarda da abinda nafada to yanzu kasan abinda zai faru dakai anjima da yamma?yace aa,sai yace ai kaima baka saniba,nace masa dama kaji nace maka nasan abinda zai faru danine nanda anjima.

Nace masa dama kai da kake cewa kana kareta to kai kanka bakasan cewa menene zai faru dakai nanda anjima ba to tunda kau hakane to ta yaya zaka iya kareta.

Amma malamai sunce kamar alal misali wanda yatafi wajen su domin yin gwaji,amma shi bai gaskata suba cewa sunsan gaibi,amma yana zuwa domin ya gwada yagani,da dai sauransu to wannan airin haka bai zama kafuri ba,amma sai dai bazaa karbi sallar saba ta kwana (40)Dalili kuwa shine fadar maaiki saw.cewa dukkan wanda yaje dan duba ya tambaye sa akan wani abu,to bazaa karbi sallar saba har ta kwana (40)Tare da cewa wajibine kuma yaci gaba da yin salla,kuma yana tuba zuwa ga Allah swt.

Wallahu taala aalam.
Ciyarwa acikin watan ramadan ta hanyar dafa abinci abayar da sadaka,ko kuma taimaka ma bayin Allah abasu sudafa da kansu yanada lada mara iyaka.Domin fadin Allh swt.acikin suratul bakra.cewa:(Misalin mutunen da suke ciyar da bayin Allah don Allah,to kamar misalin mutumin daya shuka kwara dayane ta dawa,ko masara,ko gero,wannan kwara dayan daya shuka tafito tayi tushe (7)kuma kowanne tushe yayi kwaya dari ba kwai(700)To kamar hakane ubangiji yake rubanya lada ga wanda yaciyar domin ko yabayar da sadaka,kuma Allah swt.yace yana kara rubanyawa ga wanda sama da (700)din ga wanda yaso))
Ya Allah kabamu abinda zamuyi,kuma kabamu ikonyi ameen.

ABINDA YAZAMA WAJIBI AKAN WANDA YAKE TSOHO TUKUB TUKUB,DA MACE WANDA TAKE TSOHUWA TUKUB TUKUB,DA KUMA MARA LAFIYA WANDA YAKE WANNAN RASHIN LAFIYAR TASA BAA TSAMMANIN SAMUN WARAKA,MAANA ZAI WARKE DAGA ITA!!!

Zance mafi inganci inji maluma shine,duk wanda yazama yagajiya saboda tsufa baya iya yin azumi Ramadan,ko makamancin hakan to zai ci abinci,amma ana bukatar kuma kowacce rana sai yaciyar da miskini,saboda fadar Allah swt.((Cewa ga wadannan wadanda basa iya yin azumi,maana yin sa hakan zai sa susami wahala kwarai to zasu rika bada fidya kullum shine ciyar da miskini.))Bakara aya(184).

Ansamo wani hadisi daga Adain cewa yace yaji daga Dan Abbasu (RA)Yaji ana karanta wannan ayah((وعلي الذين يطيقونه فدية طعام مسكين))Sai dan Abbas (ra)yace:Wannan ayah baa shafe hukuncin taba,abinda take nufi maana shine tana nufin tsoho tukub,da kuma mace tsohuwa tukub,idan basa iya yin azumi,to abinda zasuyi shine kowacce rana sai suciyar da miskini.

Sahihul irawaa(912) Kuma wannan hadisi danganensa ingantacce ne daga ibni Jareer.(135/2)

Hakika wannan lokacine nasamun lada,don haka dukkan ibadar da kayi zaa ninka ma ita ne,don haka wanda Allah swt.ya hore masa dama da hali,to yatai maki bayin Allah gwargwadon iya warsa.

Domin awani Hadisi manxon Allah saw.yana cewa duk wanda yaya ye ma wani muimini wani bakin ciki daga cikin bakin cikin duniya,to Allah zai yaya ye masa bakin cikin duniya da lahira.

Domin ayyukan shiga aljannah basuda iyaka,bakasan cewa wanne aikine zakayi wanda zai kaika zuwa ga aljannah ba,domin dukkan ayyukan samun lada babu abinda yakai ciyarwa lada,ko shayarwa.

Dafatan Allah yabamu ikon yi ameen.
Wallahu taala aalam.

WANNE YAFI GA MATAFIYI,DA KUMA MARA LAFIYA SHIN CIN ABINCI NE YAFI,KOKO YIN AZUMI?

Malamai sukace idan mara lafiya,ko wanda yake matafiyi yazama bazai samu wahala ba ata dalilin wannan azumin da zaiyi ahalin rashin lafiya,ko halin tafiya to yin azumi shi yafi.

Amma matafiyi,ko wanda yake mara lafiya yazama cewa idan sukayi azumi zasu sami wahala to maluma sukace a irin wannan hali cin abinci shine yafi.

Domin ansamo wani hadisi daga سعيد الحذري رضي الله عنه.
Yace:((Hakika mun kasance muna tafiya zuwa yaki alokacin watan Ramadan tare da manzon Allah saw.acikin akwai masu yin azumi,akwai kuma wadanda basa yin azumi maana suna cin abinci,domin kada su sami mushaqqa.
Kuma ahalin hakan wani baya damuwa da wani,maana mai yin azumi bai da dan uwan saba saboda baya yin azumi,shima wanda baya yin azumi bai damu da cewa suwane ai suna azumi ba,ahakan shima ranar da yaga yasami karfin jiki sai yayi,randa yaga yasami rauni sai yaaje domin hakan shine mafi kyawu.

Wallahu taala aalam.

YANA DAGA CIKIN NAUIKA NA SHIRKA WADANDA SUKA WATSU KO INA,KUMA ZUKA BAZAMA KO INA AWANNAN ZAMANI NAMU,LUNGU DA SAKO,BIRNI DA KAUYUKA.

Sune kamar haka:

(1)Nafarko shine yin Sihir.
(2)Nabiyu kuma shine Bokanci.
(3)Shine arrafa maana Yan duba.

Alal hakika yin sihir kafurcine,domin yana kafurta mai yinsa domin yana daya daga cikin abubuwa kwara (7)wadanda maaiki Allah tsira da aminci yace Allah ya gaggauta ukuba ga masu yinsa,domin sihir yana cutar wa,baya da amfani((Domin Allah madaukakin sarki yana cewa suna neman sanin abinda zai cutar dasu,kuma bazai amfane suba))Suratul bakara (102)Bayan haka Allah swt.yace :Masu yin sihir bazasu kubuta ba takowacce fuska.Dahaa ayah(79)

Bayan haka mai yin sihir ya tabbata kafiri domin Allah swt.yana cewa((Annabi Sulaimana (As)bai kafurtaba,sai dai Shaidanune suka kafurta domin sune suke koya ma mutane yadda akeyin sihir,Allah swt.yace kuma babu abinda aka saukar akan wasu mutane kwara biyi haruta,da marut,balantana har su koyar da wani mutum daya sihir,sannan suce masa mufa fiti nane,don haka kada ka kafurta)).

Hukuncin mai yin sihir,shine kisa bisa zancen maluma,kuma dukiyarsa haramunce.

Don hakane zakaga daga cikin wasu jamaa wadanda suke jahilai,ko kuma azzalumai,ko wadanda suke masu raunin imani,suna zuwa wajan masu yin sihir domin suyi masu sihir,domin su aikata wani mummunan aikin taadanci akan wasu bayin Allah,ko kuma daukar fansa.

Akwai kuma wadanda zaka ga suna zuwa su aikata wata alfahsha,koko wani aiki wanda Allah ya haramta tahanyar dalilin zuwan su wajen wannan mai yin sihir din,ko don warware sihir,ko kuma neman duniya,ta hanyar jefa mutane cikin zinace xinace,ko aikata manyan kabair,kamar yin luwadi da sunan samun duniya,kokuma kashe rai duk da sunan neman duniya,domin balain da mai sihir yake haifarwa yafi balain daake haifar wa agidan giya.

Kokuma war ware sihir,ta hanyar sihir wanda wannan badai dai bane,domin baa warkar da cuta da cuta,sai dai awarkar da cuta da magani,tahanyar komawa ga Allah swt.da neman waraka agare shi,tahanyar karanta alqurani da dai sauransu.

Bana mantawa wani abin tada hankali,kuma babban balin da ya zama ruwan dare ayanzu ubangiji Allah yamana tsari kuma shikare mu ameen.

Wato akwai wata baiwar Allah da mai gidanta yake shirin kara sabon Aure,kuma yake dauko wanda zai aura din yana kawota har gida,har wata rana takira wannan matar tasa take ce mata wlh.idan nashigo wannan gidan dole sai kinbar shi,hakan yatada mata da hankali,hakan yarika jawo matsala a tsakanin ta da mai gidanta,akoda yau she sai dai nanuna mata girman  Allah,da kuma tayi hakuri,tayi fatan alkairi,kuma tagaya ma ubangiji da muwar ta,har nace nima zan tai maketa da aduah akan samun zaman lafiya.........Ashe gaba daya hakan bai gam she taba......wlh har sai da aka wayi gari wata kawar banza tajata takai ta wajen wani makiyin Allah,da manzon sa saw.

Sai tafada masa dukkan da muwar ta akar she shine ya ummar ceta da cewa ta kwabe kayan jikinta duka saboda akwai maganin da zaayi mata,amma sai yaduba jikinta tukunna......Ya Allah kakare mu daga sharrin zamani ameen.

Bayan sundawo ne takirani take shai da man cewa itafa tayi wani abu amma bata san yazata yiba,bata san yazatayi tatubaba tafa she da kuka.........Daganan taka she wayarta,tun safe har zuwa yamma,daganan takara kirana tace wallahi malam wata kawata takai ni wajen malami ashe boka ne ban saniba,yace man nayi kaza da kaza.......Daganan takara fashewa da kuka!!!

Inna lillahi wainna ilaihi rajiun.
Daganan jikina ya hau bari,zuciyata takama makyarkyata.

Tace yanzu don Allah malam yazanyi natuba?Nace mata abinda yace kiyi kinyine tace aa,nace indai har bakiyi abinda yace kiyiba to da sauki...........Allah ya kyata ameen.

To fa makamancin wannan alamrinne yake faruwa ga dukkan matar da ta zama yar zuwa wajen bokaye da yan bori,da masu yin sihir,haka take faruwa da dukkan wanda yatare wajen yan bori,da bokaye sujefa mutum zuwa ga hallaka kuma suraba shi da uabangijinsa.Ta hanyar sa shi aikata miyagun ayyuka,wadanda Allah ya haramta.

Ubangiji Allah katsare mana imanin mu,katsare mu daga afkawa cikin hallaka,da hasara,da tabewa akan neman duniya,ya Allah kakara shiryar damu tafarki madai dai ci ameen.

SUWANE NE AZUMI YA WAJWBA AKANSU?

Wadanda azumi yazama wajibi akansu suyi shi sune kama haka:((Bisa tattaruwar maluma akan wannan cewa azumi ya wajaba ne akan mutum wanda musulmi,kuma mai hankali,kuma baligi,wanda yake lafiyayye,wanda yake kuma azaune agari))

Dan haka azumi bai zama wajibiba ga wanda yake da tabin hankali.

Azumi bai zama wajibi ba ga wanda bai balaga.

Bayan haka azumi yawajaba akan mata,amma banda macen da takeyin jinin haila,ko na haihuwa,lallai dole har sai yazama mace tana da tsarki,daga jinin haila ko na haihuwa.

Amma abinda yake tabbatar da cewa azumi ba wajibi bane ga wanda yake da tabin kwakwalwa, kuma baligi,bisa fadar maaiki saw.((Ana dauke alkalami abin rubutu akan mutane kwara (3)
(1)Ana dauke abin rubutu akan wanda yake mai tabin hankali.

(2)Ana dauke alkalami abin rubutu akan wanda yake yin barci,har sai lokacin daya falka.

(3)Ana dauke abin rubutu akan yaro karami har sai lokacin da balaga yafara mafalki.

Amma akace anso ga wanda yake majibincin wannan yaron ko mahaifansa da suyi masa umarni dayin azumi gwargwadon yadda zai iya domin ya koya,hakan kuma yin koyine da Sahabatu rasulallah.Domin sahabban manzom Allah swa.suna ummartar yaransu dayin azumi.

Ansamo wani hadisi daga Rabii dan Muawiz tace:Cewa manzon Allah saw.Akwai wata rana daakayi gari ranar ashura ya aika zuwa yan kunan alansar cewa((Duk wanda yawayi gari yana cin abinci to yacika sauran abinda yaragu na wannan ranar,wanda kuma yawayi gari yana azumi to yacigaba da azuminsa))

Bayan haka tace kuma Mun kasance munayin azumi,kuma yaranmu ma sunayi,muna sasu sunayin wasa amma da zarar muka ga yaro zaiyi kuka to sai muce yaci abinci sai muba shi abinci.

Bayan abinda yasa akace azumi yawajaba akan wanda yake lafiyayye kuma baligi,wanda zaune agari ba matafiyi ba shine,wannan ya kafune bisa fadar Allah swt.((Cewa wanda yakasance mara lafiya daga cikinku,ko wanda akan hanyar sa ta tafiya to zai iya ajiye azuminsa,amma zai gididdige kwanakin dayayi domin yin ramuwa agaba.

Amma idan mara lafiya yaga zai iya yin azumi,koko mata fiyi yaga zai iyayin azumi to wannan babu laifi hakan yayi,domin damar daaka basu na suci abinci wannan rangwamene akayi masu,domin saukaka masu,amma idan sunga suna iyawa to hakika sundauki aiki mai girma.

Wallahu taala aalam.

Ya Allah kabiya mana dukkan bukatun mu na alkairi,kayafe mana zunuban mu zahiri,da badini,manya da kanana kara bautar damu da samun jinkan ka,da rahamarka,awannan wata mai alabarka ameen.

Azumi yana daga cikin rukunnan muslunci kwara (5)

Alal hakika kamar yadda kuka sani azumi yana daya daga cikin rukunnan muslunci,kuma wajibi shi,domin yana daga cikin abubuwan wadanda muslunci ya wajabta.

Allah swt.yana fada acikin suratul bakra"Yaku masu imani hakika mun wajabta yin azumi akan ku kamar yadda muka wajabta shi ga alummar dasuka gabace ko kun kasance masu jin tsoron Allah.ayah(183)

Allah swt.yakara da cewa "Watan Ramadan shine wata wanda aka saukar da alqurani acikin sa domin yazama shiriya ga jamaa,da kuma hujjoji na shiriya da rarrabewa tsakanin abinda yake dai dai,da kuma wanda ba dai dai,tsakanin bata da kuma shiriya,tsakanin gaskiya,da kuma karya.....yakara da cewa dukkan wanda ya halarci wannan wata yana mai lafiya,yana mai hankali,kuma wanda yake baligi to ya azumce shi.bakra ayah(185).

Ansamo wani hadisi daga dan Ummar (ra)yace:Manzon Allah saw.yace:((Angina addinin muslunci ne abisa abubuwa kwara (3)

(1)Mutum ya shaida babu wani abu da ya cancanta a bauta masa sai Allah swt.shi kadai.

(2)Shine dole ka tabbatar cewa Annabi Muhammad saw.Manzon Allah ne.

(3)Kuma shine tsayar da sallah,maana kabatar da sallolin farilla.

(4)Da kuma bayar da zakka.Ga wanda Allah swt.yaba shi iko,da hali.

(5)Ziyartar dakin Allah,da kuma azumtar watan Ramadan.

Ansamo wani hadisi daga Abu huraira (ra)Yace:manzon Allah saw.Yace:Dukkan wanda ya azumci watan Ramadan yana mai imani,da kuma kyatata zaton sa ga Allah to Allah zai gafarta masa zunubansa da suka gabata.

Anrawaito wani hadisi shima daga Abu Huraira (ra)yace:Hakika maaikin Allah tsira da aminci su tabbata agare shi yace:Allah mai girma da daukaka yace:Kowanne aikin lada wanda dan adam zaiyi to nasane wannan,amma banda azumi,azumi wannan nawane,nine zanbada sakamakonsa da kaina.Azumi kuma kariyane,kuma garkuwane,yace idan aka wayi gari dayan ku yana azumi to kada yarika yin maganganu na alfahsha,maganganu marasa amfani,kada yarikayin ayyuka marasa amfani,ko wasanni marasa anfani,yace idan wani mutum yazage ka alhali kana azumi,ko yanemi da fitina,ko yane meka da fada to kace masa ni azumi nike,ka mai maita masa hakan har sau biyu.

Yace narantse da wanda rayuwata take a hannunsa yace warin bakin mai azumi awajan Allah ranar alkiyama yafi kam shin Almiski,kuma mai azumi yana da abubuwan farin ciki kwara biyu,wadanda zaiyi farin ciki dasu:Sune Alokacin da yayi buda baki zaiyi farin ciki da haka,bayan haka kuma da lokacin da ya hadu da  Allah swt.nan ma zai yi farin ciki da wannan azumin da yayi.

Domin akwai wani hadisi daaka samo daga Sahal dan Saad (ra)Yace:Hakika manzon Allah saw.yace acikin aljannah akwai wasu kofofi anace masu rayyan,wadannan kofofi masu azumine kadai zasu shigesu aranar alkiyama,babu wani mutum daya da zaa bari ya shiga wanda ba mai azumi ba.Yace zaarika yin kira ana cewa .......Ina masu azumi...ina masu azumi?Daganan zasu tashi babu wani mutum daya da zaa bari ya wuce wannan kofa sai su kadai kawai,kuma da zarar sun gama shiga sai arufe kofar bawanda zaa bari yakara shiga daga nan.

Ya ubangiji kasa muna daga cikin wadanda zasu shiga wannan kofar ameen.

Wednesday, 1 March 2017

Bayani dangane da abinda yashafi habbatisauda, da kuma manta.

Muujizati Shifaa

Muujizati shifaa :littafin daya tattara bayanai akan yadda zaa iya neman waraka tahanyar amfani da
Habbatirashad
Tafarnuwa
Albasa
Zuma
 
Wanda wani bawan ALLAH balarabe mai suna Abul-fidaa MUHAMMAD azzat MUHAMMAD Aarifi yarubuta.
Allah yasaka masa da alkairi Ameen.

Bayani ko wata hikaya dangane da wani bawan ALLAH wanda Allah madaukakin sarki yajarabce shi da gudawa wanda taki tsayawa har kusan wata (6)wanda yake dayane daga cikin mazauna kasar masar.

Tsira da aminci su tabbata ga shugaban Annabawa da manzanni, shine shugabammu mai sammu mai kaunar mu, kuma abin kaunarmu Annabi MUHAMMAD saw. Tare da Iyalan gidan sa baki daya, da sahabban sa.
************************************

Dafarko abinda wannan bawan ALLAH yafara cewa.......

<<<<<<#Al-habbatisauda_dakuma_zuma>>>>>>

Yace hakika wadannan abubuwan kwara biyu #Habbatisauda da kuma zuma yace wallahi sunada matukar faida da kuma babbar falala da daraja agareni?????????? Badan komai yafadi hakaba sai don tsabar Faidar su daya gani sunyi masa, shi ne yasa shi yake ganin cewa kamar dama don shi kadai aka yo su!!!

Yace nakasan ce nakamu da gudawa mai tsananin gaske har tsawon wata shidda bata yanke ba, yace naje wajen likitocin daban daban suna rubuta man magungunan dake tsayar da gudawa naje nasiyo nasha, amma da zarar nagama sha kafin zuwa wani lokaci sai takara dawowa yadda take kamar bansha maganiba.........

Yace haka naci gaba da kasance wa acikin wannan halin, bayan haka wani likitan gona, kuma masani ta abangaran abinda yashafi jini, da fitsari, shi ma yadebi jini na, da kuma fitsari na domin ya gwada yaga cewa wacce irin cuta ce wanda take haifar man da wannan matsala
Bayan wannan likitan yagama bincike akai sai ya tabbatar da irin matsalar da take daymuna daga nanne nafara jin dadi cewa matsalata tazo karshe!!!

Sai dai akar she wani babban abinda yakara tada mun da hankali shine, bayan dana gama amfani da magungunan daya bani, kawai sai wannan gudawa takara dawowa kamar yadda take!

Nakoma wajan wannan likitan daganan yafada man cewa lallai babu makawa akwai abin lura dangane da uwar hanjin ka, da babban hanjin ka (large intestines) wata kila kodai akwai ciwo aciki ajikin sa, kokuma kuraje acikin ajikin su!!!

Ikon Allah daganan ne babban bakin ciki yasameni, da kuma babbar damuwa wanda tasanya na dimauce, amma duk da haka batasa na yanke tsammani daga rahamar ALLAH ba dangane da samun waraka daga wannan matsalar tawa!

Daganan nafara nazari dakuma tunani cewa kodai naje naga babban  
Likita Dr. Hassan Alhijari, likitan daya kware bangaran Cutuka wadanda baagane kansuba, dakuma bangaran matsalar Ciwon zuciya.

Amma shi wannan likitan yana yima marsa lafiyar sane magani da itatuwa, da kuma ganyayyaki, na muslunchi, da kuma asalin zuma, da hanyoyin neaman waraka wanda mutanan kasar China suke amfani da Ita.
Domin shi baya amfani da magungunan wadanda aka sarrafa su da ainufin chemicals, sai dai lokaci lokaci.

Danaje wajensa sai nadauki kwalbar zuma, yana kallona sai yace ga maganin ka nan a hannun ka kana rike dashi!!!

Kabar magani a gefen ka kana ta wahala kawai!!!

     Daga gobe na hore ka da kasha karamin kofin zuma dukkan bayan awa (3)haka zaka cigaba da yi har zuwa kwana daya.

Bayan haka sai kasamo #Huran_albabunaj katafasa sai katace kazuba cokali daya na zuma kasha kafin kaci abinci daawa daya...... Ikon daganan sai naji nafara samun yanayi mai dadi lafiya tafara samuwa kadan, amma dai wannan gudawa bata tsayaba baki daya.


Daganan sai wani abokina yabani wannan littafin mai suna ((Muujizati shifaa))

 
Daganan kawai sai gashi nasami abinda nabata acikin sa wajen neman sa, Yace sai nasamo man #Habbatisauda kawai kai tsaye nakama yin magani dashi,kamar yadda aka fada acikin wannan littafin, daganan cikin Ikon Allah gudawa tatafi baki daya bayan kwana uku dafara amfani da man habbatisauda,wanda yake na kwashe sama da wata biyar inafama  da Ita bata tsayaba.

Yace :Daganan nacigaba da cin kowanne kalar abinci, nasami lafiyar jikina fiye da shekarun da suka gabata.

Yace alal hakika bazan iya suffan ta irin yadda habbatisauda tazama magani mai ban mamaki wajan magance mun dukkan rashin lafiya ta ba.

Yace wannan abinda najarraba, don haka nabada ta sadaka ga dukkan wani mara Lafiya wanda yarasa magani daga Ciwon sa bayan duk yayi iya bakin kokarin to ga hanya sadaka. 

Yace Allah shine wanda yake me tabbatsr da shaida akan abinda nafada. 

Dafatan ALLAH yasaka masa da alkairi Allahumma Ameen. 

Rahamaniyya Islamic medicine Centre Funtua. 

Twitter @likitanci. 

Whatsapp 08152753609.

rahamaniyyaharbalmedicine.blogspot.com

Guzurin mamaci bayan mutuwar sa!!! (3)

Guzurin mamaci bayan mutuwar sa!!! Na (3)
************************************

Hadisi ya tabbata acikin Sahihi MUSLIM (RA) daga hadisin #Jarir_dan_Abdullah Yace :Manzon ALLAH saw. Yace:((lallai dukkan wanda ya tabbatar da wani aiki na alkairi kyakyawa acikin muslunci to bashakka yanada lada, da lada ga dukkan wanda Yayi koyi dashi na wannan kyakyawan aikin dakayi, amma batare da antauye ladar wadanda sukayi koyi da shiba, wannan kyakyawan abun alkairin daka aikata ba, aa ladar da zaa baka kaida kafara gaba tar da wannan abun alkairin,ko aikin daban, suma wanda sukayi aiki dashi ladar su daban, domin baa cikin ladar su zaa diba abaka ba na koyin dasukeyi dakai!!!

Haka kuma dukkan wanda yafara asassa wani mummunan aikin nasharri, ko sabon Allah madaukakin sarki, ko wani fasadi to zaa bashi mummunan sakamakon wannan aikin nasa daya kirkira.

Bayan haka kuma zaarika dora masa wani zunubin ga dukkan wanda yayi koyi ko yaaikata irin wannan aikin sharri daka gina ka kirkira, duk wanda yayi koyi dakai abayanka to sai anrubuta maka zunubi kaima akai, tare da cewa zunubin wanda yai koyi dakai daban, kuma zunubin da zaa rubuta maka daban na koyi da sukayi dakai, batare da antauye nasu zunuban ba.!!!!

Ubangiji Allah yamana tsari yakare mu Allahumma Ameen.

Alal hakika ire iren wadannan maanoni na wannan hadisin Antarosu dayawa daga manzon ALLAH saw. Ta fuskoki dadama, Kuma wadanda suke kyawawa,masu inganci.

Sahihi Muslim (3/1255)Babi wanda yake bayani abinda dan adam yake samu na lada bayan mutuwar sa.

Hakika wannan dalili yake nuna mana cewa kan magana na manzon ALLAH saw. Bazaa taba kashe wata rai bisa zalunci ba, face sai Allah madaukakin sarki yadora wani zunubin akan dan adam nafarko wanda yafara sunnanta kisan kai, domin shine wanda yafara gabatar
da wannan mummunan aikin!!!

To idan wannan bayani yakasance tafuskar yin azaba, da kuma ukuba, ko sakamako, to alal hakika abinda yake mafifici akai shine wajan samun falala, da kuma samun lada, ko sakamakon,na irin haka.

Maana idan kafara akata wani aikin sharri to dukkan wanda yayi koyi dakai abayanka to kana da zunubi...... To tunda Hakane wannan yanuna mana cewa kenan ina ga wanda yafara gabatar da wani aiki na alkairi kenan shine yafi cancanta da kuma dacewa asami sakamako.

Wallahu taala aalam.

Ya Allah kabamu Ikon kirkira abin alkairi, ko aiki na alkairi wanda yan bayan mu zasu amfana dashi, domin muma mu amfana dashi koda bayan mutuwar mu Allahumma Ameen.

Treat your sick by giving sadaqah!!!


Treat you sick by giving sadaqah!!!

1 - From Abu Umamah -Radi Allaahu anhu-who said: the Messenger of Allaah -sallAllaahu alayhi wa sallam- said:‘Treat your sick by giving Sadaqah (charity).’

[Collected in Saheeh al-Jamia’ No. 3358 & declared Hasan by Albaani]

2 - From Ubadah bin Saamitt who said I heard the Messenger of Allaah -sallAllaahu alayhi wa sallam- saying: ‘There is no person who is afflicted with a wound on his body, and he gives charity due to that, then Allaah Expiates from him the like of what he gave in charity.

[Collected by Ahmad & Albaani declared it to have an authentic Isnaad in Saheehah No. 2273]

3 – A man asked Abdullaah bin al-Mubarak -Rahimullaah- about ulcers that had sprung out on his knee for about seven years, and he tried to treat it with various treatments, he had asked doctors but to no avail. So Ibn Mubarak said: ‘Go and dig a well in a place where people need water, indeed I hope that there springs up water there, and by that you stop bleeding.’  The man did that and Allaah Ta’ala Cured him.’

[Taken from: ‘Seerah ‘Alaam’ 8/407]

Al-Bayhaqi quoted a story of our Shaykh al-Haakim Abu Abdullaah -Rahimullaah- who was afflicted with ulcers on his face, and he had tried a number of treatments but they did not go away, and it remained like that for nearly a year.

He then asked the teacher, Imam Abu Uthmaan as-Sabooni to make Dua’ for him in one of his gatherings on Friday, so he made Dua’ and many of the people with him said Ameen.  When it came to the next Juma’ a woman came to the gathering and left a brief message saying that she had gone back home and exerted herself in making Dua’ for al-Haakim Abu Abdullaah that night, and that she had seen the Messenger of Allaah -sallAllaahu alayhi wa sallam- in her sleep, and it was as if he was saying to her: tell Abu Abdullaah to distribute water amongst the Muslims.

I came with that message to al-Haakim, and he ordered that a watering place be built at the door of his home, when they had finished building it, he ordered for water to be poured into it and ice placed into that water, and then the people began drinking from that water.  Not a week had passed by, except that it was obvious that his health had been restored, and the ulcers had ceased. His face had become better than it was before, and he lived like that for a number of years.’

[Collected in ‘Saheeh Targheeb wa Tarheeb’ No. 964 Albaani declared it to be Saheeh Maqtu, 1/p.568]

4 - Abu Tahir as-Silafee said in ‘Mua’jam as-Safr’: I heard Abu Hasan Ali bin Abu Bakr Ahmad bin Ali the scribe of al-Minzi in Damascus saying: I heard Abu Bakr al-Khabazi (d. 449A.H.) in Nisaboor saying: I became sick with a very dangerous illness, and a righteous neighbor of mine saw me and said: ‘Utilize the saying of the Messenger of Allaah -sallAllaahu alayhi wa sallam-: ‘Treat your sick by giving Sadaqah (charity).’

It was summer time, and I bought many watermelons, and a group of poor people and children got together and ate them, then they raised their hands to Allaah –Azza wa Jal- and they made Dua’ for me to be cured.  I swear by Allaah I had not reach the morning except that I regained complete health from Allaah -Tabaraka wa Ta’ala.

[Seerah ‘Alaam 18/44, Tareekh al-Islaam]

5 - al-Barzali (d. 841A.H.) said in his Fatwa (5/612): Ibn Rushd was asked about the saying of the Messenger of Allaah -sallAllaahu alayhi wa sallam-: ‘Treat your sick by giving Sadaqah (charity).’ Is it authentic or not? And what does it mean? And if a person becomes sick and treats his illness with all types of medicines and they did not benefit him, then what is the way of giving Sadaqah as a medicine?

He answered:

‘I do not remember this text (narration) in any of the authentic collections of narrations, however, if it is authentic, then the meaning is an encouragement to visit the sick, because it is from the obligatory rights from the Sunnah that it is upon a Muslim that he visit a Muslim if he becomes sick.

As for the saying ‘The Muslim is a brother of a Muslim, he encourages him to say the testification at the time of death, and he visits him when he is sick, and advises him when he is absent or if he has to testify.’ As for visiting him then this is a good deed, and every good deed is Sadaqah, since it has a connection with the sick person and visiting him brings happiness to him, and just like making Dua’. There is no doubt that there is hope that the Dua’ will be answered and he will be cured.  Therefore, it does benefit him as a type of medicine, due to the saying of the Messenger -sallAllaahu alayhi wa sallam-: ‘He who sent down the illness also sent down the treatment.’

Al-Barzali said: some of our shaykhs from al-Qarawan understood this to have an evident meaning, namely that if a person gives Sadaqah on behalf of the sick, and that he requests the person whom he gave Sadaqah to, to make Dua’ for the sick then it is hoped that he will be cured, due to the saying of the Messenger -sallAllaahu alayhi wa sallam-: ‘The supplication of one of you for his brother in his absence is answered.’

6 – ad-Dooree narrated in ‘Tareekh’ and al-Bayhaqi in ‘Shu’ab al-Eemaan’ from Ibraheem an-Nakhai who said: ‘that the Companions used to regard giving Sadaqah as a means of repelling oppression.’

7 – From Hudayfah -Radi Allaahu anhu- that the Prophet -sallAllaahu alayhi wa sallam- said:

‘A fitnah (trail) which a man faces with regard to his family, his wealth, his own self, his son and his neighbor is expiated by fasting, prayer, charity, enjoining good and forbidding evil.’

[Collected by Bukhari & Muslim]

8 – Shamsuddeen Muhammad bin Abee Bakr Ibn Qayyim aj-Jawzeeyah (d.751 A.H.) -Rahimullaah- said:

‘Indeed Sadaqah has an amazing effect in repelling different types of trials and tribulations, even if the charity was given by an evil person, or an oppressive person, in fact even if it was given by a non-Muslim! Indeed Allaah Ta’ala repels different types of trials and tribulations due to giving Sadaqah.  This is a matter which is well-known to the scholars and the general folk, and all of the people on the earth can associate with this fact because they have experienced it.’

[Taken from: ‘al-Wabil as-Sayyib’ p.63]

9 – Shamsuddeen Muhammad bin Abee Bakr Ibn Qayyim aj-Jawzeeyah (d.751 A.H.) -Rahimullaah- said:

‘There are types of medicines which can treat illnesses which the minds of the senior doctors cannot comprehend, and that which their sciences, experiences and measurements cannot reach. These are the medicines of the heart and soul, and the strength of the heart, its dependence upon Allaah and trust upon Him and seeking refuge in Him. Prostrating and feeling in dire need of Allaah and humbling oneself for Allaah. Likewise giving Sadaqah (charity), making Dua’, repentance and seeking forgiveness, being good to the creation, aiding the distressed and liberating from grief and unhappiness.

Indeed these types of medication have been used by various nations, who are upon different religions and communities, and they found that they had an effect in the treatment of illnesses, which even the sciences of the most knowledgeable doctors could not reach, and they have no experience nor measurement of it. We have indeed experienced these matters a great deal and as others have, and we have seen what ordinary medicine can and cannot do.’

[Taken from: ‘Zad al-Ma’ad’ 4/11-12]

Guzurin mamaci bayan mutuwar sa kashi na (4)

Manya manyan dalilai da suka zo daga cikin alqurani, da sunna  da ijmain maluma, da kuma kawaid na Sharia wadanda suke nuni akan wadanda suke mutu suna samun lada tahanyar ayyukan wadanda suke raye......

Kamar Allah madaukakin sarki yafada acikin suratul hashar aya(10)

Allah madaukakin sarki yace "wadannan wadanda suke biyo bayansu suna cewa ya ubangijin mu kayi mana gafara, tare da yan uwan mu wadanda suka rigaye mu wajan yin imani...... "Allah yana yabon mu tahanyar yima bayin Allah wadan da suka riga mu yin imani tun farko ,sune sahabban manzon ALLAH saw. Domin haka manzon ALLAH saw. Yafada fiyayyun alumma sune wadanda sukayi zamani dani..... To wannan dalili yanuna cewa dalilin rigayar mu imani shi yasa ubangiji yasanya suna amfana da istigfarin mu, da kuma neman gafara da muke yi muna hadawa dasu aciki.
والذين جاءوامن بعدهم ربنااغفرلنا ولاخواننا الذين سبقونا بالإيمان....... الا ية.
Don haka indai kayi istigfari to suma suna da nasu rabon aciki na abinda suka kafa na alkairi, kuma nasu ba zai sa atauye nakaba.

Kamar yadda maluma sun tattaru basuyi sabani ba wajan yima mamaci aduah tahanyar roka masa gafara alokacin daake yima sa SALLAH.

Hadisi ya tabbata daga sunan na Abu Dawud (rahimahullah) Daga hadisin na Abu huraira (RA) yace :manzon ALLAH saw. Yace ((Idan zaku sallaci mamaci to kukebanta wajan yi masa addua,tahanyar roka masa gafara.

Bayan haka Anrawaito wani hadisi acikin Sahihi Muslim daga hadisin Aufi dan MALIK (ra) yace:wata rana manzon ALLAH saw. Yanayin sallatar wata gawa, sai muka kiyaye wani abu daga cikin adduoin dayarika yi, yana cewa "((Ya ubangiji  kayi gafara agare shi, kajikan sa, kayi masa rangwame, ka kuma saukaka masa, ka girmama masaukin sa, ka yalwata masa shi, kawanke shi daga dukkan zunubai, da ruwa, da kankara, da sanyi ka kuma tsarkake shi daga kurakuransa daya aikata sukoma fari fat,kamar yadda muke wanke farin tufafi daga datti, kuma ka canza masa gida wanna yafi gidan sa na duniya, ka canza masa Iyalan sa fiye da iyalinsa dayabari a duniya, ka canza masa mata fiye da matar sa ta duniya, ya Ubangiji muna rokonka kashigar dashi aljanna, kayi masa kariya daga azabar kabari.

Dafatan ALLAH ubangiji yayafe mana dukkan kurakuranmu zahiri ,da badini, Ya Allah ka kyatata karshen mu kasa mucika da imani. Ka gafar ta ma dukkan mamatan mu musulmi maza da mata Allahumma Ameen.